‘Yan Boko Haram sun kashe sojoji 3 da fararen hula 8 a Monguno

Mayakan Boko Haram sun kashe sojoji uku da wasu fararen hula takwas tare da raunata wasu da dama a garin Monguno da ke jihar Borno, bayan  sun kutsa cikin dakarun sojojin da wata mota mai dauke da bamabamai. Wannan harin na zuwa ne bayan  kwanaki 10 da janye sojojin Chadi da ke taimakawa takwarorinsu wajen […]

‘Yan Boko Haram sun kashe sojoji 3 da fararen hula 8 a Monguno

Mahara

Mayakan Boko Haram sun kashe sojoji uku da wasu fararen hula takwas tare da raunata wasu da dama a garin Monguno da ke jihar Borno, bayan  sun kutsa cikin dakarun sojojin da wata mota mai dauke da bamabamai.

Wannan harin na zuwa ne bayan  kwanaki 10 da janye sojojin Chadi da ke taimakawa takwarorinsu wajen yakar Wani bangare na ‘yan kungiyar Boko Haram ISWAP da ke yankin tafkin Chadi a Areawacin jihar Borno.

A wani rahoton da sojojin suka fitar na cewa, a jiya Alhamis an yi musayar wuta tsakanin Sojojin da ‘yan Boko Haram a shataletalen Monguno.