’Yan daba sun bude wa masu zabe wuta a Bayelsa

Wasu ’yan bangar siyasa sun bude wa jama’a wuta tare da sace kayan zabe a yayin da ake gudanar da zaben gwamnan jihar Bayelsa.

’Yan daba sun bude wa masu zabe wuta a Bayelsa

Wasu ’yan bangar siyasa sun bude wa jama’a wuta tare da sace kayan zabe a yayin da ake gudanar da zaben gwamnan jihar Bayelsa.

’Yan bangar siyasanan sun kai harin ne a wasu rumfunan zabe a kananan hukumomin Ija ta Kudu da kuma Sabgama, insa suka rika harbe-harbe suna tafiya da kayan zabe.

Maharan sun fatattaki masu zabe suka kwashe kayan zaben a yankin Agorogbene, rumufanan zabe masu lamba 6, 7 da 8 gunduma ta 11 da kek Karamar Hukumar Ijaw ta Kudu.

Masu zabe sun nemin yin fito-na-fito da ’yan bangar siyasan, amma suka mayar da martani da harbe-harbe.

Da misalin karfe 9 na safe wasu bata-garin sun kai hari a cibiyar tattara sakamakon zabe inda suka yi awon gaba da kayan zaben biyar daga cikin mazau bakwai.

Venezuela na ci gaba da samun tallafi bayan mummunar girgizar ƙasa

PRP ta yi fatali da shirin kafa ’yan sandan jihohi

Sojoji sun ceto mutum uku da aka yi garkuwa a Zamfara

An umarci bankuna su rufe asusun masu alaƙa da ta’addanci