’Yan fashi sun yi hatsari a hanyarsu ta tserewa

’Yan fashin sanye da kayan ’yan sanda sun yi hatsari a hanyarsu ta kai motar Legas. 

’Yan fashi sun yi hatsari a hanyarsu ta tserewa

‘Yan Sanda a yayin bincike

Wasu ’yan fashi sanye da kayan ’yan sanda sun yi hatsari a motar da suka yi fashinta, a garin tserewa da ita.

Bayan kwace motar, kirar Toyota Camry, a hannun mai ita da karfin bindiga, ’yan fashin sun shafe daruruwan kilomitoci domin tserewa da ita su kai ta Legas, amma suka yi mummunan hatsari.

“Mai motar da ya taso takanas daga Jihar Ondo ya ce mutum biyar ne sanye da kayan ’yan sanda suka kwace ta a hannunsa da karfin bindiga, suka yi wurgi da shi, sannan suka tafi da ita,” inji Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ogun, inda motar ta yi hatsari da ’yan fashin.

Kakakin Rundunar, Abimbola Oyeyemi ya ce motar satar ta yi hatsari da uku daga cikin ’yan fashin da ke cikinta ne a garin Ode Remo na Karamar Hukumar Remo ta Arewa a Jihar ta Ogun.

Ya ce daya daga cikin ’yan fashin ya mutu, ragowar biyun kuma sun samu munanan raunuka, amma an garzaya da su zuwa asibiti, inda ’yan sanda ke tsare da su.

Oyeyemi, ya ce DPO na Ode Remo, ya tabbatar da samun rahoton cewa motar da ta yi hatsarin an yi fashinta ne.

Ya ce an Kwamishinan ’yan sandan Jihar ya sa a mayar da ’yan fashin  zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka domin kammala tattara bayanai, a gurfanar da su a kotu.

HOTUNA: Yadda bikin Takutaha ya gudana a Kano

Zaɓen Gwamna: APC ta kama hanyar lashe zaɓen Edo

Zaɓen Edo: INEC ta dakatar da tattara sakamako

Zaɓen Edo: Magoya bayan PDP sun fara zanga-zanga