’Yan fashin teku sun sace jirgin fasinja mutum 11 sun ɓace a Ribas
Jami’ai sun ce an kuɓutar da tara daga cikin fasinjojin yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don ceto sauran.
![’Yan fashin teku sun sace jirgin fasinja mutum 11 sun ɓace a Ribas ’Yan fashin teku sun sace jirgin fasinja mutum 11 sun ɓace a Ribas](https://aminiya.ng/wp-content/uploads/2025/02/Fashin-jirgin-ruwa.jpg)
OOS_001
Wasu da ake zargin ’yan fashi ne sun yi awon gaba da wani jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji 20 a hanyar ruwa daga Bonny zuwa Okrika a Jihar Ribas.
Sai dai jami’ai a ƙaramar hukumar Bonny ta ce ta kuɓutar da tara daga cikin fasinjojin yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don ceto sauran.
- Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace
- Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da rai
Shugaban Ƙaramar hukumar Bonny, Hon Anengi Barasua Claude-Wilcox ya ce, an ceto mutanen tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro.
Claude-Wilcox a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Boma Waribor ya fitar a ranar Juma’a, ya ce direban jirgin fasinja ya saɓa wa ƙa’idar wucewa ta kilomita 10, wanda haramtacciyar hanya ce ga direbobin kwale-kwalen fasinja.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Tattaunawar tsaro da shugaban ƙaramar hukumar Bonny, Anengi Barasua Claude-Wilcox ya yi, ya nuna cewa an yi fashin wani jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji 20 da ke kan hanyarsa ta zuwa Bonny da yammacin ranar Alhamis a yankin Isaka da ke Ƙaramar Hukumar Okrika.
“Duk da haka, ya kamata a lura da cewa an gano mutane tara aka dawo da su Fatakwal ta hanyar sa hannun jami’an tsaro na gwamnati a kan lokaci, waɗanda a halin yanzu suka ƙara ƙaimi wajen ceto sauran fasinjoji 11.
“Ya kamata a lura cewa binciken farko ya nuna cewa, direban jirgin ya bijirewa ƙa’idar hanyar kuma ya wuce kilomita 10, hanyar ruwan da aka haramta ga direbobin Jirgin ruwan fasinjoji.