`Yan Najeriya zasu samu walwala a mulkin PDP – Obi

Mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP Mista Peter Obi, ya ce, jam`iyyar zata sanya ‘yan Najeriya annashuwa da walwala idan suka lashe zaben takarar shugaban kasa da za a yi ranar 16 ga  Fabirairu 2019. Obi ya bayyanawa manema labarai hakan ne a jiya Talata a wani taron siyasa da aka yi a […]

`Yan Najeriya zasu samu walwala a mulkin PDP – Obi

Mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP Mista Peter Obi, ya ce, jam`iyyar zata sanya ‘yan Najeriya annashuwa da walwala idan suka lashe zaben takarar shugaban kasa da za a yi ranar 16 ga  Fabirairu 2019.

Obi ya bayyanawa manema labarai hakan ne a jiya Talata a wani taron siyasa da aka yi a Awka babban birnin jihar Anambra.

Obi ya kara da cewa, jam’iyyar PDP zata farfado da tattalin arzikin Najeriya da mulkin APC ta durkusar, kuma ci gaba da zaben APC a karo na biyu za a sake raunata kasar.

 

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta