’Yan sanda sun cafke ƙasurgumin ɗan fashi da makami a Kano

Rundunar ta cafke ɗan fashin yayin da yake ƙoƙarin tserewa a kan babur.

’Yan sanda sun cafke ƙasurgumin ɗan fashi da makami a Kano

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta sanar da cafke wani ƙasurgumin ɗan fashi da makami tare da ƙwato bindiga ƙirar AK-47 guda biyu da kum alburusai 47.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce sun kuma samu kuɗi kimanin Naira miliyan 4.9 a hannun wanda ake zargin.

A ranar Litinin da misalin ƙarfe 2 na dare ne, wani mazaunin garin Yandadi a ƙaramar hukumar Kunchi da ke Jihar Kano, ya kai rahoton cewa ’yan fashi sun kai masa hari a gidansa, sannan kwashe masa kuɗi Naira miliyan 15.

Duk da tarzomar da ake fama da ita a Kano sakamakon zanga-zangar yunwa, kwamishinan ’yan sandan jihar, Salman Dogo Garba, ya bayar da umarnin bin sahun waɗanda suka aikata laifin.

Da misalin ƙarfe 6 na safiyar ranar Talata ne, ‘yan sanda suka kama ƙasurgumin ɗan fashin mai suna Hassan Iliya, mai shekara 35 mazaunin garin Alhazawa a ƙaramar hukumar Musawa ta Jihar Katsina.

Ya shiga hannun rundunar ne yayin da yake ƙoƙarin tserewa a kan babur.

An samu bindiga ƙirar AK-47 guda biyu tare alburusai 47 da kuma kuɗi har N4,986,000.00 a cikin wata jakarsa.

Rundunar ta ce a yanzu haka tana ci gaba da gudanar da bincike.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan