’Yan sanda sun ceto mutum 3 daga hannun ’yan bindiga a Nasarawa

An sace mutanen ne a kan hanyar Kaduna zuwa Keffi.

’Yan sanda sun ceto mutum 3 daga hannun ’yan bindiga a Nasarawa

‘Yan sanda

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, sun kai samame maɓoyar masu garkuwa da mutane tare da ceto mutum uku a Ƙaramar hukumar Karu.

Waɗanda aka ceton su sun haɗa da Abdulsalam Shuaibu, Sani Shuaibu, da Blessing Okorie, waɗanda aka sace a kan titin Kaduna zuwa Keffi.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Ramhan Nansel, ya ce maharan sun tafi da su zuwa daji.

Bayan samun rahoton, SP Zaks Wambai, DPO na yankin, ya jagoranci tawagarsa don yin bincike.

Tawagar ta gano maɓoyar maharan inda suka fatattake su, tare da ceto waɗanda aka sace.

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Nasarawa, CP Shetima Jauro Mohammed, ya yaba wa jami’an kan nasarar da suka samu.

KADVS ta daƙile yunƙurin sace yara da ceto wasu a Zariya

Gwamnatin Tinubu na yunƙurin hana ni yin takara — Peter Obi

An gurfanar da ƙarin mutum 17 bisa zarginsu a kisan malama

An kama matashi ɗauke da hannun mutum da bindigogi