’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
An ceto yaran ne a wani samame da ’yan sanda suka kai wurin da masu garkuwar suka je karbar kuɗin fansa.
Rundunar ‘yan sandan Borno
’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su, masu shekaru hudu da biyar, a Jihar Borno.
An ceto yaran ne a yayin wani samame da ’yan sanda suka kai a Ƙaramar Hukumar Jere, inda masu garkuwar suka je karbar kuɗin fansa.
Sanarwa da ASP Nahum Kenneth Daso, kakakin rundunar ya fitar ta ce, bayan sun sami rahoto a ranar 4 ga Disamba cewa yara uku sun bace, washegari masu garkuwar suka sako ɗaya daga cikin yaran da takardar neman naira miliyan 10 domin sakin sauran biyun.
A ranar ce jami’an rundunar suka kai samame a wurin da aka ware don karɓar kuɗin fansar.
Ganin hakan masu garkuwa da mutanen, suka farga da wannan tarko da aka musu nan da nan suka yi watsi da yaran suka gudu cikin duhu.
An ceto yaran ba tare da wani rauni ko biyan kuɗin fansa ba, kuma sun sake haɗuwa da iyalansu, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano waɗanda ake zargi.
Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Yobe, Naziru Abdulmajid, ya ba da umarnin zurfafa bincike kuma ya umurci jami’an rundunar da su qarfafa sintiri, su gudanar da ayyukan bincike mai tsauri, da kuma ci gaba da gudanar da ayyukansu don rage yawaitar aikata laifuka a baya-bayan nan.
Hukumar tsaron ta kuma yi kira ga mazauna yankin da su kasance cikin shiri da kuma bayar da rahoton ayyukan da ake zargi, tare da samar da lambobin tuntuɓar gaggawa don hanzarta kai xauki.