’Yan sanda sun fara bincike kan kisan Janar ɗin Soja a Abuja

Rundunar ta ce za ta kamo maharan tare da gurfanar da su.

’Yan sanda sun fara bincike kan kisan Janar ɗin Soja a Abuja

Kwamishinan Rundunar ‘Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, Abuja Benneth Igweh, ya bayar da umarnin fara binciken kan kisan da wasu da ake zargi ‘yan fashi suka yi wa wani tsohon ɗin Janar a gidansa da ke Abuja.

Maharan sun kutsa gidan Birgediya Janar Uwem Udokwere (mai ritaya), inda suka yi masa kisan gilla.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, ASP Josephine Adeh ta fitar, ta ce an kashe tsohon janar ɗin a gidansa da ke rukunin gidajen Sunshine da ke unguwar Lokogoma a eanar Asabar.

Kwamishinan ya kuma jajanta wa iyalan marigayin, tare da yin alƙawarin farautar waɗanda ke da hannu a kisan nasa.

‘’Za mu yi duk abin da ya dace don tabbatar da kama maharan domin gurfanar da su a gaban kotu domin su girbi abin da suka shuka,” in ji sanarwar.

Aminiya ta ruwaito yadda wasu ’yan fashi da makami sun kashe Janar ɗin a gidansa.

Mutum biyu sun shiga hannu kan zargin sace mahaifiyar Rarara

An ƙone jabun magunguna na N985m a Kano

Sarkin Kaltungo ya koya jama’arsa dabarun noman rogo na zamani

Kasuwar Karu da ke Abuja ta yi gobara