Yana fuskatar daurin shekara 37 kan zagin karen sarki

Wani dan kasar Thailand na fuskantar daurin shekara 37 saboda tuhumarsa da aibata karen Sarkin kasar, a wani sharhi da ya yi a shafin sadarwarsa na intanet, al’amarin da ya saba wa sauraran dokokin kasar da ta kare martabar Sarki. Mahukunta sun tsare mutumin wanda ma’aikacin wata masana’anta ne, mai suna Thanakorn Siripaiboo a gidansa […]

Yana fuskatar daurin shekara 37 kan zagin karen sarki
Yana fuskatar daurin shekara 37 kan zagin karen sarki

Wani dan kasar Thailand na fuskantar daurin shekara 37 saboda tuhumarsa da aibata karen Sarkin kasar, a wani sharhi da ya yi a shafin sadarwarsa na intanet, al’amarin da ya saba wa sauraran dokokin kasar da ta kare martabar Sarki.
Mahukunta sun tsare mutumin wanda ma’aikacin wata masana’anta ne, mai suna Thanakorn Siripaiboo a gidansa da ke wajen birnin Bangkok, a makon da ya wuce, inda suka tuhume shi da laifin rubuta munanan kalamai” ya baza a shafin intanet, game da Tongdaeng, wato karen Sarki Bhumibol Adulyadej, kamar yadda jaridar New York times ta ruwaito shekaranjiya Laraba.
Gwamnatin mulkin soja da ta yi juyin mulki a kasar a bara, har yanzu ba ta fayyace kowane irin laifi Thanakom ya yi ba.
Kare Tongdaeng, wanda sunansa ke nufin farin karfe, Sarkin na matukasr kaunarsa, kamar yadda mujallar Times ta ruwaito. A makon da ya wuce aka yi fim din Khun Tongdaeng, wanda ke nuni da rayuwarsa a cikin zayyana da aka tsakuro daga littafin tarihin Sarki Bhumibol, da aka rubuta a shekarar 2002 game da karensa.
Wannan tuhuma da ake yi wa Thanakum ita ce ta baya-bayan nan da aka ce an keta dokar kare martabar Sarki, wadda masana suka ce a ’yan kwanakin nan sai kara fadada take yi. Kuma a Disamban bara an kama wasu dalibai da suka yi ikirarin zagin Sarki, bayan sun gudanar da wani wasan kwaikwayo a kan rayuwar Sarkin.
’Yan jarida sun ruwaito a shafukan twiter game da rahoton mujallar Times, cewa, tuhumnar laifuffukan d aake yi Thanakun ba ta fito a jaridun kasar Thailand ba.