ECOWAS ta fara sabon taro kan daukar matakin soji a Nijar

Masu juyin mulkin Nijar sun yi watsi da barazanar ECOWAS na ɗaukar matakin soji, inda suka nada ministoci

ECOWAS ta fara sabon taro kan daukar matakin soji a Nijar

Shugabannin ƙasashen Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Yammacin Afirka (ECOWAS) sun fara taro kan ɗaukar matakin soji da za su yi bayan cikar wa’adin kungiyar ga masu juyin mulkin kasar Nijar.

ECOWAS wadda shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu yake jagoranta tana yin wannan zama ne bayan cikar wa’adin da ta ba wa sojojin da suka yi juyin mulkin na dawo da Shugaba Mohamed Bazoum kan kujerarsa.

Masu juyin mulkin Nijar sun yi watsi da barazanar ECOWAS na ɗaukar matakin soji, inda gabanin taron ƙungiyar sojojin suka kafa majalisar ministoci mai mutum 21.

Sojojin sun kuma rufe iyakokin da asararurin samaniyar ƙasar tare da barazanar yaƙar duk wanda ya nemi yin shisshigi a harkokin ‘cikin gudana kasarsu.

An fara sana’ar hayar Fawa-bank a Kano

’Yan sanda sun kama fasinja ya ɓoye bindiga a cikin burodi 

An kama fasto kan kashe ’yar shekara 13 da duka

KADVS ta daƙile yunƙurin sace yara da ceto wasu a Zariya