Mahara sun kashe sojoji 3 da ’yan banga 2 a Nasarawa

Wasu da ake zargin ’yan sa-kai ne a sun kashe sojoji uku da ’yan banga biyu a yankin Karamar Hukumar Toto a Jihar Nasarawa.

Mahara sun kashe sojoji 3 da ’yan banga 2 a Nasarawa

Wasu da ake zargin ’yan sa-kai ne a sun kashe sojoji uku da ’yan banga biyu a yankin Umaisha  da ke Karamar Hukumar Toto a Jihar Nasarawa.

Ana zargin ’yan sa-kan sun kai wa jami’an tsaron harin kwanton bauna ne a yankin Umaisha, lamarin da ya haifar da zaman dar-dar.

Aminiya ta gano cewa wasu mahara sun kai hari a kwanan nan a kauyen Okudu inda suka kakkashe jama’a.

Kasa da mako guda kenan bayan a ranar 1 ga watan Fabrairu wasu mahara sun kashe mutane uku suka kona kadarori na miliyoyin kudi a kauyen.

An girke sojoji a kauyukan Katakpa da Okudu ne domin samar da zaman lafiya, sakamkon rikicin da aka samu tsakanin kauyukan biyu.

Hotunan yadda Zaɓen Gwamnan Edo ke gudana

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu