’Yar Shaikh Ibrahim Nyass ta rasu

Sayyada Maryam Nyass ta sadaukar da rayuwarta kacokan wurin hidimar Alkur’ani

’Yar Shaikh Ibrahim Nyass ta rasu

Sayyada Maryam Nyass

Allah Ya yi wa Sayyada Maryam Shaikh Ibrahim Inyass rasuwa a Kasar Senegal.

Sayyada Maryam diya ce ga shahararen malamin Musulunci na duniya kuma jagoran Darikar Tijjaniya, Marigayi Shaikh Ibarhim Nyass dan kasar Senegal.

Ana yi wa Sayyada Maryam lakabi da Hadimar Alkur’ani wanda ta saudaukar da rayuwar kacokan wurin hidimar Alkur’ani Mai Girma.

Sayyada Maryam ita ce ta assasa cibiyar haddar Al’kur’ani ta Darul Kur’an a shekarar 1975.

A karkashin cibiyar, ta gina makaranta mai dalibai 1,600 a Dakar, babban birnin kasar Senegal.

Makarantar ta yaye dimbin mahaddata Alkur’ani daga kasar Senegal da makwabta irinsu Gambia da Guinea Bisau.

Marigayiyar ta kuma gina makarantar Majma’u Sheikh Ibrahim Nyass Alta’alimi a shekarar 1984 a Dakar.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta