Yau za a fara jigilar maniyyatan Najeriya zuwa Saudiyya

Maniyyata kimanin 65,000 daga Najeriya za su sauke farali a aikin Hajjin 2024

Yau za a fara jigilar maniyyatan Najeriya zuwa Saudiyya

Maniyatta aikin hajji

A Laraba za a fara jigilar maniyyatan Najeriya zuwa kasar Saudiyya domin sauke farali a aikin Hajjin bana.

Jirgin sahun farkon zai tashi ne a Kebbi da maniyyatan jihar, kamar yadda Hukumar Aikin Hajji ta Najeriya (NAHCON) ta sanar.

Kimanin maniyyata 65,000 ne ake sa ran za su sauke farali daga Najeriya a aikin Hajjin bana.

Hukumar ta ce ana sa ran tashin jiragen maniyyata biyu a kullum daga filayen jiragen sama 15 da aka ware a fadin Najeriya, har sai an kammala kai su Kasa Mai Tsarki.

NAHCON ta bayyana cewa tana sa ran kammala kwashe maniyyatan Najeriya zuwa Saudiyya kafin ko a ranar 10nga watan Yuni, 2024.

Aminiya ta ruwaito shugaban NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, yana cewa maniyyatan za su shafe akalla kwanaki hudu a birnin Madina domin yin ziyara kafin su wuce Makkah domin yin Umrah da aikin Hajji.

A ranar Laraba 14 ko Alhamis 15 ga watan Yuni ake sa ran fara aikin Hajjin 2024, inda za a yi Hawan Arafa a washegari.

Alhazai za su yi Hadaya da jifan farko hadi da Babbar Sallah a washegari.

Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine

Madalla da hutu ga ’yan makaranta domin azumi

Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala

Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya