Zaɓen Edo: Ana ci gaba da ƙirga ƙuri’u

Rahotanni sun bayyana cewar an kammala kaɗa ƙuri’u, yanzu haka an fara ƙirga sakamakon zaɓen a matakin ƙananan hukumomi.

Zaɓen Edo: Ana ci gaba da ƙirga ƙuri’u

An rufe rumfunan zaɓe bayan kammala kaɗa ƙuri’u a zaɓen Gwamnan Jihar Edo da aka gudanar ranar Asabar.

Tuni aka fara ƙirga ƙuri’u a matakin rumfunan zaɓen.

Rahotonni sun nuna cewar an gudanar da zaɓen ba tare da matsala a wurare da dama a faɗin jihar.

A yanzu hankula sun fara karkata kan cibiyoyin tattara sakamakon zaɓen, domin tattara sakamakon a matakin ƙaramar hukuma kafin daga bisani a tafi matakin jiha.

Manyan jam’iyyun siyasar jihar guda uku; PDP, APC da kuma LP na son ganin ɗan takararta ya lashe zaɓen jihar.

Zaɓen Edo: Yadda aka kama masu sayen ƙuri’a da ’yan daba

Sarakunan Nijar sun kai wa Gwamnatin Yobe ziyarar jaje

Ɗan majalisa ya yi jinjina kan naɗa Danyaya Sarkin Ningi

’Yan Sanda sun kama gungun ’yan fashi 7 a Katsina