Za a binne gawarwaki 60 da ba a gano ’yan uwansu ba a Kaduna

Gwamnatin Jihar Kaduna za ta binne gawarwakin wasu mutane 60 da ba a san masu su ba a makabartar Tudun Wada

Za a binne gawarwaki 60 da ba a gano ’yan uwansu ba a Kaduna

Kabarin da aka sanya gawar Marigayiya Maryam Bayero

Gwamnatin Jihar Kaduna za ta binne gawarwakin wasu mutane 60 da ba a san masu su ba.

Sashin Lafiya na Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu zai dauki gawawwakin don binnewa a a Makabartar Layin Bashama da ke unguwar Tudun Wada.

Mataimakiyar Sashin lafiya na Karamar Hukumar Kaduna ta kudu- Asmau Saidu Adamu ta sanar cewa za a binne gawarwakin ne a ranar Juma’a 17 ga watan Nuwamba da muke ciki.

“Za a dauko gawarwakin ne daga Asibitin Gwamna Awan zuwa Makabartar Bashama Road, karkashin jagorancin Kwamishinar Lafiya ta Jihar Kaduna, Umma K Ahmed da Shugaban Asibitin Gwamna Awan, Dokta Gebriel Brown,” inji ta.

Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP

Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa

Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno 

’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci