Za a biya inshorar N13bn ga ’yan sandan da suka mutu

’Yan Sanda 318,319 da suka rasu ne za su ci gajiyar shirin tsakanin shekarar 2022 da 2023

Za a biya inshorar N13bn ga ’yan sandan da suka mutu

Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ta amince da biyan Naira biliyan 13.3 a matsayin inshora ga ’Yan Sandan Najeriya da suka mutu.

Ministan Harkokin ’Yan Sanda, Maigari Dingyadi, ya ce jami’ai 318,319 ne za su ci gajiyar shirin tsakanin shekarar 2022 zuwa 2023.

A cewarsa, an samar da shirin inshorar ne don karfafa wa ’yan sanda gwiwa a aikin da suke yi babu dare, babu rana don kare rayuka da dukiyar ’yan kasa.

Ya bayyana haka ne ga manema labarai bayan kammala taron Majalisar a Fadar Shugaban Kasa ranar Laraba.

Taron Majlisar ya gudana ne karkashin jagorancin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.