Za a ci gaba da rufe iyakar Najeriya da Benin
Shugaban hukumar shige da ficen kayayyaki na kasa (kwastam), Alhaji Abdullahi Dikko Inde ya ce hukumar ba za ta bari a rika shigo da kayayyaki daga bakin iyakar Najeriya da jamhuriyar Benin ba, har sai jami’an kwastam na kasar ta Benin sun mutunta yarjejeniyar kasa-da-kasa da aka shinfida.Shugaban ya ce bai yiwuwa a ce kasashen […]

Shugaban hukumar shige da ficen kayayyaki na kasa (kwastam), Alhaji Abdullahi Dikko Inde ya ce hukumar ba za ta bari a rika shigo da kayayyaki daga bakin iyakar Najeriya da jamhuriyar Benin ba, har sai jami’an kwastam na kasar ta Benin sun mutunta yarjejeniyar kasa-da-kasa da aka shinfida.
Shugaban ya ce bai yiwuwa a ce kasashen biyu su cimma matsaya a kan dokokin junansu, amma sai jami’an kasar ta jamhuriyar Benin su koma daga gefe suna yin yadda suka ga dama.
Ya ce ya kai wannan batun gaban shugaban Najeriya da ministar kudi kuma ya bayyana musu irin yadda jami’an kasar ta jamhuriyar Benin suke wasa da yarjejeniyar da aka cimma, wanda idan ta kama a rufe bakin iyakar, sai a rufe.
Shugaban kwastan din yana magana ne sa’ilin da yake ganawa da masu fiton kayayyaki da ke Jihar Legas, yayin da suke kokawa domin ganin an bude bakin iyakar Najeriya da jamhuriyar Benin har na tsawon watanni biyu kuma hakan ya kawo musu cikas wajen neman abin zaman gari.
Da aka tambaye shi ko yana sane da jami’ansa masu kwace kayan mutane ko bayan sun biya kudin ka’ida na fito, sai Alhaji Dikko Inde ya ce duk jami’in kwastam din da aka kama yana karbe kayan mutane, bayan an biya kudin ka’ida na fito, ya kuka da kansa, domin za a kore shi daga aiki, idan kuma an samu har ya karbi kudi, sai an gurfanar da shi gaban alkali kafin a kore bakin aikin.
Alhaji Dikko Inde ya ce hukumar kwastan ta samar da tsarin aiki mai kyau, wanda ya ba ma’aikata dukkan hakkokinsu tare da inganta muhallinsu da duk wani abu da ka iya kyautata aikinsu, don haka ba su da kowace irin hujja ta karbar hanci da rashawa. yace samar da aikin su cikin sauki yasa hakan ya kara samar da kudin shiga ga hukumar ta kwastan.
Da kuma yake bayanin sabon tsarin aikinsu ta amfani da na’ura mai kwakwalwa, sai ya ce kayan da za ka jira cikin sati ko fiye, yanzu cikin awoyi 54, ka karbi kayanka kuma daga yanzu ba za a iya yin fasa kwabri ta hanyar shigowa da kayayyakin da ba a amince da su ba, sabanin yadda ake yi a da.
Alhaji Dikko Inde ya ce kafin ka shigo da kaya, sai an nuna maka an yarda a shigo da su ko a’a.
Daga karshe ya bayyana jin dadinsa na yadda hukumar ta yi nasarar karbar aikinta na karbar haraji daga hannun wasu kafanionin kasashen waje, wadanda suka dade suna tatsar Najeriya kuma tana biyan su kudin aiki ko sun karba yadda ya dace ko kuma akasi aka samu. “Najeriya na da wadatattu kuma gogaggun ma’aikatan kwastan da suka san wannan aikin, amma kuma sai aka dauka aka danka wa wasu kamfanonin kasashen waje”. Inji shi.