‘Za a iya raba mutum miliyan 100 da talauci nan da 2025’
Tilas ne shugabanni da kasashe su mike wajen dakile abubuwan da suke haddasa talauci.
Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres
Majalisar Dinkin Duniya ta ce za a iya fitar da mutum miliyan 100 a fadin duniya daga kangin talauci nan da shekarar 2025.
Majalisar ta ce duk da barazanar koma-bayan tattalin arziki da ake fuskanta, abu ne da zai yiwu a raba mutum miliyan 100 da talauci nan da shekarar 2025.
- Mutum 14 sun rasu, gidaje 50 sun salwanta a ambaliyar Gombe
- Kotu ta yanke mata daurin rai-da-rai kan mutuwar mijinta
Sakamakon binciken da majalisar ta fitar kan taulaci, ya nuna za a iya rage talaucin da ake fama da shi, a kuma samar da sababbin dabaru a fagen yaki da talaucin don taimaka wa gwamnatoci wajen cimma wannan kudiri.
Majalisar ta fitar da sakamakon binciken ne a Ranar Yaki da Talauci ta Duniya, wadda akan yi ran 17 ga Oktoban kowace shekara.
Ta ce, domin cim ma nasara a wannan yaki, tilas ne shugabanni da kasashe su mike tare da daukar ingantattun matakan dakile abubuwan da suke haddasa talauci a cikin al’umma.