Za a yi ambaliyar ruwa a Kano da wasu jihohin Arewa 12 – NEMA

Hukumar ta ce dukkan jihohin a Arewacin Najeriya suke

Za a yi ambaliyar ruwa a Kano da wasu jihohin Arewa 12 – NEMA

Ambaliyar Ruwa

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana wasu yankuna 50 a Jihohin Arewa 13 da ta ce za su fuskanci ambaliyar ruwa cikin kwanaki 4 masu zuwa.

A cewar hukumar, ana hasashen fuskantar ambaliyar ce daga ranar Laraba, 13 zuwa Lahadi 17 ga watan Satumban 2023.

Ko’odinetan hukumar a Jihar Legas, Ibrahim Farinloye, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a Legas, ranar Laraba.

A cewar sanarwar, a Jihar Kano, ana hasashen samun ambaliyar a yankunan Sumaila da Kunchi.

A jihar Kebbi kuwa, akwai yankin Argungu, sai Katsina mai yankunan Bindawa, Jibiya, Kaita da cikin birnin Katsina.

Sauran yankunan su ne Kwantagora da Mashegu da New Bussa a jihar Neja, sai Kosubosu a Kwara.

“A Zamfara, akwai yankunan Kauran Namoda da Shinkafi; sai Bauchi mai yankunan Bajoga, Darazo, Kirfi, Azare, Jama’are, Itas, Misau; Taraba na da yankunan Bali, Donga, Lau, Serti, Mutum-Biyu, Yorro, yayin  da a Borno akwai yankunan Briyel, Biu, Dikwa, Kukawa,” in ji shi.

Ya kuma ce a jihohin Adamawa kuwa, yankunan da ake hasashen fuskantar ambaliyar su ne Ganye, Mubi, Demsa, Jimeta, Mayo Belwa, Numan, Shelleng, da Song.

Farinloye ya kuma ce a Yobe, akwai yankunan Dapchi, Gashua, Geidam, Kanamma, Machina da Potiskum da su ma ke cikin barazana.

A Gombe ma, NEMA ta ce za a iya samun ambaliyar a Nafada, sai Jigawa mai yankunan Dutse, Gumel, Gwaram da Miga.

Ko’odinetan ya kara da cewa sakamakon ƙaruwar yawan ruwa a Kogin Kwara da na Binuwai, ana shawartar mazauna yankunan da ke makwabtaka da kogunan har zuwa jihar Bayelsa da su ma su dauki matakan kariya. (NAN)

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda