Za mu hukunta masu hannu a harin Tudun Biri —Hafsan Tsaro

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christoper Musa ya ce rundunar za ta hukunta duk sojan da aka samu da laifi a harin Tudun Biri

Za mu hukunta masu hannu a harin Tudun Biri —Hafsan Tsaro

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christoper Musa

Babban Hafsaon Tsaron Najeriya, Janar Christoper Musa ya ce rundunartsaro za ta hukunta duk wanda ta samu da hannu a harin da jirgin soji a kauyen Tudun Biri a Jihar Kaduna.

Janar Musa ya sanar a ranar Juma’a cewa da zarar rundunar ta kammala bincike kan harin, duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.

ya shaida wa manema labarai a Hedikwatar tsaro da ke Abuja cewa babu yadda za a zura ido wani ya yi irin wannan aika-aika ba tare da an hukuna shi ba.

A cewarsa, “a aikin soja ba ma kare masu laifi, saboda haka za mu yi komai a fili, babu rufa-rufa.

“Mun sha hukun dakarunmu da ke rundunar Operation Hadin Kai, wasunsu koun soji ta yanke musu hukuncin dauri a kurkuku.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan