Za mu kara soke lasisin wasu masu hakar ma’adanai a bana — Alake

Ana fama da matsalar masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a Najeriya.

Za mu kara soke lasisin wasu masu hakar ma’adanai a bana — Alake

Masu hakar ma’adanai

Gwamnatin Tarayya ta sanar cewa a wannan shekarar ta 2024 za ta karbe lasisin karin wasu kamfanoni masu hakar ma’adanai a kasar.

Ministan Albarkatun Kasa, Dokta Dele Alake ne ya bayyana hakan a sakonsa na sabuwar shekarar 2024 a jiya Litinin a gidansa da ke Jihar Legas.

Mista Alake ya kara da cewa gwamnati tana gayyatar masu zuba jari daga kasashen ketare a fannin hakar ma’adanan, don haka zamanin kin biyan gwamnati hakkinta ya wuce.

Ana fama da matsalar masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a kasar, da masu lasisin da ba sa biyan kudaden haraji a fannin hakar ma’adanan.

Idan ba a manta ba, a watan Nuwambar bara ne Gwamnatin Najeriyar ta sanar da soke lasisin kamfanonin hakar ma’adinai 1,633 daga hannun wadanda ba su biya kudaden da ya kamata su biya gwamnati da suka hada da haraji ba.

Sai dai tun kafin gwamnatin ta dauki wannan mataki, wasu daga cikin jihohin kasar daga cikinsu har da Jihar Neja suka dakatar duk wasu harkokin hako ma’adanan.