Za mu taimaka wa Najeriya ta gyara matatun manta – Saudiyya
Gwamnatin kasar Saudiyya ta yi alkawarin zuba jari domin farfaɗo da matatun man Najeriya da kuma taimaka wa gwamnati ta aiwatar da tsare-tsaren daidaita darajar Naira. Yariman Saudiyya, Muhammad Bin Salman ne ya yi alkawarin yayin tattauna da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu a gefen taron kasar da kasashen Afirka da yake gudana a Riyadh, babban […]
Yarima mai jiran gadon Masarautar Saudiyya, Muhammad Bin Salman
Gwamnatin kasar Saudiyya ta yi alkawarin zuba jari domin farfaɗo da matatun man Najeriya da kuma taimaka wa gwamnati ta aiwatar da tsare-tsaren daidaita darajar Naira.
Yariman Saudiyya, Muhammad Bin Salman ne ya yi alkawarin yayin tattauna da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu a gefen taron kasar da kasashen Afirka da yake gudana a Riyadh, babban birnin kasar.
- Yakin Gaza: Tinubu ya bukaci a gaggauta tsagaita wuta
- Gaza: Iran ta yi barazanar shiga yakin Isra’ila da Hamas
Saudiyya ta kuma yi alkawarin tallafa wa Najeriya, ta hannun Babban Bankin Najeriya (CBN), domin a farfaɗo da darajar Naira.
Yarima Muhammad, a cikin wata sanarwa da Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya kuma yabawa manufofin tattalin arzikin da Shugaba Tinubu yake aiwatarwa.
A cewar Yariman na Saudiyya, ƙasar shi ta ƙagu ta ga Najeriya tana bunkasa a karkashin Shugaba Tinubu, musamman a matsayinta na jagaba a Afirka.