Za mu yafe wa ’yan Boko Haram idan suka dawo da ‘yan matan Chibok lafiya – Buhari

Wakilinmu  da ke Washington DC  ya samu  damar tattaunawa da  shugaba Buhari lokacin da ya je taron Majilisar dinkin duniya a New York a kan al’amura daban-daban da suka shafi Najeriya. Ga yadda hirar ta kasance: Aminiya:Ranka ya  dade  yaya kake ganin batun cim ma muradun karni da aka  shinfida, anya nahiyar Afrika za ta […]

Za mu yafe wa ’yan Boko Haram idan suka dawo da ‘yan matan Chibok lafiya – Buhari

Wakilinmu  da ke Washington DC  ya samu  damar tattaunawa da  shugaba Buhari lokacin da ya je taron Majilisar dinkin duniya a New York a kan al’amura daban-daban da suka shafi Najeriya. Ga yadda hirar ta kasance:

Aminiya:Ranka ya  dade  yaya kake ganin batun cim ma muradun karni da aka  shinfida, anya nahiyar Afrika za ta iya  cim ma lokacin da  aka  shata?
Buhari: kasashen Afrika kowa ya ji a jikinsa, babu abin da mu  Afrika  muke so  illa zaman lafiya  da  wadata, domin ta  kowace  irin gwamnati  ce kuma ta kowace  irin jam’iyya  ce, fatanta  shi ne  ta  tabbatar  da kasarta  ta zauna  lafiya, an samar  wa  al’umma aikin yi, kuma  ya  zamanto  suna  iya  noma  abincin da  za su  ci  har ma  su  sai da wa  wadansu  kasashe  daban. Kuma ta fuskar tsaro  suna  zaune  lafiya, kana  akwai wutar lantarki,  akwai hanyoyi  masu kyau, akwai ruwan sha,  akwai  makarantu,  akwai  asibiti.Wannan shi ne burin kowace  irin gwamnati, balle  ma na  kasashenmu  masu  tasowa.
Aminiya:A  da ana da muradu 8, yanzu an mayar da su 12, yaya kake kallon wannan lamari, ba za a bar  nahiyar Afirka a baya ba?
Buhari:To kasashen Afirka an riga  an tsere  musu, duk wanda ya fi ilmin zamani,  musammam abin da ya shafi kimiyya, ya zo ya yi ma’aikatu da yawa, ya sama wa mutanensa aiki, ya tabbatar  yana  noma  abin da zai ci ba tare da sai ya saye ba, ya tabbatar cewa  jami’an tsaronsa  an horar  da su suna  son kasarsu,  suna aiki ba da son rai ba, an yi musu bariki,  yaransu  suna zuwa  makaranta ba tare  da  damuwa ba,idan ba su da lafiya suna  zuwa asibiti, albashi yana zuwa a kan kari  yadda ya kamata, shi ne zama lafiya da ci gaba.
Aminiya:A cikin jawabinka a  Majilisar dinkin duniya ka ce Najeriya ta mayar da hankali wajen yaki Boko Haram, amma sai ga shi an yi  taro  game  da tsaro wanda ya shafi Najeriya  ba ka wurin kuma ba wakilinka, me ya faru?
Buhari:To mutum ba sai ya sani ba  zai je, ko ka je abin da  ba ka da masaniya ne  a kai?
Aminiya:Wato ba a sanar daku ba?
Buhari:Ba a sanar da mu ba,  yaya  za ayi mu sani kuma mu ki  zuwa? yanzu cikin mako  guda, cikin satin da aka rantsar  da ni na je Nijar da Chad, ba ya da kirana da  aka yi a Jamus da kuma manyan kasashen  duniya  masu  arziki su 7, kuma naje  kamaru,  amma  sai da na dawo  taro  da  kasashen nan 7  na tafi Kamaru, haka kuma na je jamhuriyar Benin, kuma har wayau mun shirya  taro  na shugabbanin  sojoji  na  wadannan kasashen,wato Benin da Chadi da Kamaru Nijar da Najeriya, muka hadu  a Abuja. Bayan wannan taron sai  kuma  ministocin tsaro  suka  hadu, kana mu shugabannin kasashen muka  hadu. To me za mu yi fiye da  wannan? sai dai  kawai  mu zo domin mu cim ma  matsaya a kan yadda  za mu  tafiyar  da yankin Chadi ga kasashen da ke kewaye da tafkin na Chadi.
Aminiya:Wani lokaci  can baya ka ce ba za a wuce watan Satumba ba za ka fitar da sunayen ministocinka,  amma  ga shi sai da aka  kai daf  da karshen watan sannan ka  aika  sunayen, me ya faru?
Buhari:To kar ka manta cewa ‘yan majilisa sun yi,  hutu idan muka aika wane ne  za mu aika  mawa? Da  suka dawo  ba ka ga mun aika ba, yanzu muna jira ne mu ji wadanda  ba su  yarda  da su ba  da  kuma dalilin da ya sa  ba su  yarda  da su ba sai  a cire  su.
Aminiya: A cikin jawabin da ka yi ka zargi wadansu kasashe da kawo  wa Najeriya tarnaki  a yakin da take yi da cin hanci da rasahawa, ko za ka kara haske  kan abin da kake  nufi?
Buhari:Sani kowa  ne jiragen ruwan da suke  zuwa su  dauki mai  a Najeriya su kai shi inda  za a sai da duk jiragen na kasashen waje ne kuma akwai doka na jiragen ruwa cewa duk kayan  da  suka  dauka za a rubuta inda suka dauki kayan da kuma inda zasu kai su. Sai ya zamana ciki binciken da muka fara yin a satan man Najeriya akwai jiragen ruwan da  suke daukar mai amma ba za su tafi  inda aka yi za su kai man ba,  sai a cikin teku za a juye wa  wani jirgi  daga nan shi kuma sai ya yi  gaba da man. Kuma idan aka je  aka sayar sai a bude  ajiyar banki a waccan kasar  da jirgin da  aka juye mawa  ya kai, alhali  daga  Najeriya ba kasar  da aka yi  za a kai man ke nan ba, kuma ba  a ciki ajiyan Najeriya za a sanya kudin ba, kodayake ba kasar  da suka ce  ke nan za su kai man ba,  sai  dai a ajiye  kudin a cikin ajiyar  bankin wadansu mutane, kuma sau tari  wadansu  kasashen suna  sane. Shi ya sa na ce  abin da na ce.
Aminiya: Ina maganar ‘yan matan Chibok ya kwana ne,  domin wasunsu  da  suka  samu tserewa suna  nan Amurka?
Buhari: To wadannan da  suka  zo  nan Amurka ni ban san wanda  ya kawo  su ba, amma  tun da  ‘yan Najeriya ne, domin ko  sun yi amfani  da  takardar iznin shiga  wata  kasa ta Najeriya,  wato Fasfo, to  har yanzu ‘yan Najeriya ne.Yanzu  kikarin da  wannan gwamnati  take yi  shi ne  ta san sauran ‘yan matan nan a  ina suke? Wane hali  suke  ciki?saboda  wannan yana  sawa yadda  sojoji suke  nema su yi da su ‘yan Boko Haram muna  damuwa kwarai  da  gaske kada su kai  yadda  idan aka  fada wa  ‘yan Boko Haram su cutar  da su, shi ya sa  ake magana  da  shugabannin ‘yan Boko Haram wadanda   aka sani, cewa idan za su ba mu ‘yan matan nan gaba daya kamar  yadda  suka  dauke  su  kuma  cikin lafiyarsu, to mu za mu yafe musu  laifin da  suka  yi wa  Najeriya, duk da dai  sun kashe  ‘yan Najeriya  da  yawa.
Aminiya: Me  gwamnatin za ta yi domin rage zaman banza da shaye-shaye a tsakanin matasa?
Buhari:To na farko  dai maganin shaye-shaye shi ya sa ake da  ‘yan sanda  da kuma hukumar yaki da shan miyagun kwayoyi (NDLEA) inda ake da kwararru,  idan magungunan mara sa  tasiri ne ko masu cutarwa ne muna magana  da su manyan kasashen da  ake  kawo  wadannan muggan kwayoyin cewa duk wanda aka samu da  wannan laifin  babu afuwa za a hukunta shi  daidai  da  yadda  doka  ta tanada, kuma muna fata iyaye suna  samun  lokaci suna  sa wa ‘ya’yansu ido,  ba zuwa  makaranta ba su dawo a ba su  abinci  ba, a’a kamata  ya yi iyaye  su gane  shin wadanne  irin abokai  ne  ‘ya’yansu  suke  da su? kuma su taimaka wa  gwamnati, su  ba ta bayanin inda  suka  san ana sayar  da wadannan kwayoyin masu yi  wa  mutane illa,  ko  kuma  su sanar da jami’an hukumomin nan masu  wannan aiki don a kama  su,  a san daga  ina  suke  kawo  wadannan kwayoyin.To yanzu matsalar ta kai ga cewa  har  su  masu  shan kwayoyin sune  ke yin kwayoyin  da kansu ko  kuma  su rika shan magungunan tari  wanda ya  wuce  ka’ida  domi kawai  su yi maye,  wannan abu ne mai wahala,  amma ya kamata  iyaye  su ma su shigo  cikin wannan  lamari  ba wai  gwamnati za a bari da kashin mahaukacin kare  ba.