Zaben 2019: EFCC ta yi gargadin cewa akwai dalolin jabu
Hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC ta yi gargadin cewa akwai dalolin jabu da ke yawo a cikin kasar don shirin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a yi ranar Asabar. Mukaddashin shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu ya fitar da sanarwar bayan bayanan sirri da […]
Hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC ta yi gargadin cewa akwai dalolin jabu da ke yawo a cikin kasar don shirin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a yi ranar Asabar.
Mukaddashin shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu ya fitar da sanarwar bayan bayanan sirri da hukumar ta samu yayin shirin gudanar da zaben ranar Asabar.
Hukumar EFCC ta bukaci ‘yan canji su yi taka-tsantsan a harkar kasuwancin su.