Zaben Kogi: An gano ma’aikatan zabe 30 da suka bace
Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC) ta ce, an gano ma’aikatan Hukumar 30 da aka sanar da bacewar su, a wasu rumfunan zabe na zaben Gwamnan jihar Kogi da aka yi jiya Asabar. Rotimi Lawrence Oyekanmi, Sakataren watsa labarai na Shugaban INEC Farfesa Mahmood Yakubu. Rotimi Lawrence, ya ce a yanzu ma’aikatan suna […]
Tambarin Hukumar Zabe ta Kasa INEC
Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC) ta ce, an gano ma’aikatan Hukumar 30 da aka sanar da bacewar su, a wasu rumfunan zabe na zaben Gwamnan jihar Kogi da aka yi jiya Asabar.
Rotimi Lawrence Oyekanmi, Sakataren watsa labarai na Shugaban INEC Farfesa Mahmood Yakubu.
Rotimi Lawrence, ya ce a yanzu ma’aikatan suna cikin koshin lafiya ba tare da wani rauni ba, kuma sun isa gidajensu.