Zakanya ta kashe mai ba ta abinci a Iran

Zakanyar ta tsere ita da mijinta.

Zakanya ta kashe mai ba ta abinci a Iran

Zakanya

Wata Zakanya ta kashe mai kula da ita a wani gidan ajiyar namun dawa a kasar Iran yayin da yake ciyar da ita da wani Zakin abincin rana.

Zakanyar ta kubuce daga keji lokacin da ya ke sa musu nama ta taga, sannan ta gudu da wani Zakin da ke zaman mijinta.

Kamfanin dillancin labaran IRNA da ke kasar Iran, ya bayyana cewa marigayin mai suna Esfandani yana da shekaru 40, sai dai tuni aka kama dabbobin biyu bayan mai aukuwar ta auku.

’Yan sanda da masu gadi sun kama zakunan biyu bayan ’yan sa’o’i suna neman hanyar fita daga gidan dabbobin wanda yake a tsakiyar birnin Arak, kimanin kilomita 200 Kudu maso yammacin Tehran babban birnin kasar Iran.

Hukumomi na gudanar da bincike kan kashe mutumin da Zakanyar ta yi, ko da yake ana yawaita samun kubucewar namun jeji daga gidajen adana dabbobi a kasar Iran, kuma galibi ana zargin rashin matakan tsaro a wasu gidajen adana namun jejin na haifar da barazana.

Bayanai sun ce gidan kula da namun dajin na Arak na cikin mafi girma a kasar Iran.

Zaɓen Edo: Yadda aka kama masu sayen ƙuri’a da ’yan daba

Sarakunan Nijar sun kai wa Gwamnatin Yobe ziyarar jaje

Ɗan majalisa ya yi jinjina kan naɗa Danyaya Sarkin Ningi

’Yan Sanda sun kama gungun ’yan fashi 7 a Katsina