Zan bar Liverpool a karshen kakar wasanni —Sadio Mane

Akwai alaka mai karfi tsakanin dan wasan Senegal din da FC Bayern Munich.

Zan bar Liverpool a karshen kakar wasanni —Sadio Mane

Sadio Mane

Sadio Mane ya yanke shawarar barin Liverpool, ya shirya komawa wata kungiyar bayan kwashe shekaru masu yawa a Anfield – amma sai nan gaba kungiyar za ta tabbatar.

Akwai alaka mai karfi tsakanin dan wasan Senegal din da FC Bayern Munich – sai dai har yanzu ba a cimma wata matsaya ba abin da zai bai wa sauran kungiyoyi damar daukar dan wasan idan suna bukata.

Dan wasan ya buga wa Liverpool wasa 269, ya kuma ci kwallo 120 ya kuma taimaka aka ci 48.

Dan wasan wanda kungiyarsa ta yi rashin nasara har sau biyu a hannu Real Madrid a wasan karshe na Kofin Zakarun Turai, ya ci kofina shida da Liverpool

An sanya dokar hana fita a wasu yankunan Taraba

Jami’an NSCDC sun daƙile harin ’yan bindiga a Kano

Matsalar Tsaro: Ku sayi makamai don kare kanku — Sarkin Argungun

Mai juna biyu na wata 8 ta shigar da ƙarar neman saki