Zan biya ma’aikata sabon albashi – Gwamnan Jigawa
Gwamnan jihar Jigawa Mohammed Badaru ya yi alkawarin biyan sabon mafi karancin albashin ma’aikatan jihar. Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da Kungiyar kwadago ta kasa NLC reshen jihar Jigawa a yau Talata don tabbatar wa kungiyar cewa, a shirye Gwamnan yake ya kaddamar da sabon albashi mafi karanci. Bayan tattaunawa kan […]
Gwamna Muhammad Badaru Abubakar
Gwamnan jihar Jigawa Mohammed Badaru ya yi alkawarin biyan sabon mafi karancin albashin ma’aikatan jihar.
Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da Kungiyar kwadago ta kasa NLC reshen jihar Jigawa a yau Talata don tabbatar wa kungiyar cewa, a shirye Gwamnan yake ya kaddamar da sabon albashi mafi karanci. Bayan tattaunawa kan batun karin albashi mafi karanci na Naira 30,000 kamar yadda kungiyar Kwadago ta bukata.