Zan tsaya takarar shugaban Chadi — Mahamat Deby

Ni ne ɗan takarar shugaban ƙasa na gamayyar jam’iyyun United Chad Coalition.

Zan tsaya takarar shugaban Chadi — Mahamat Deby

Shugaban Gwamnatin Sojin Kasar Chadi, Janar Mahamat Idriss Deby Itno. (Hoto: Denis Sassou Gueipeur/AFP)

Shugaban mulkin sojin Chadi, Mahamat Idriss Deby Itno, ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen da za a yi a watan Mayu mai zuwa.

Mahamat Idriss Deby, ya bayyana haka ne a wani jawabi da ya yi ranar Asabar a N’Djamena, babban birnin ƙasar.

A jawabin da ya yi, ya ce “Ni, Mahamat Idriss Deby Itno, ne ɗan takarar shugaban ƙasa na gamayyar jam’iyyun United Chad Coalition a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2024.”

Hukumar zaɓen ƙasar ta ce za a gudanar da zagayen farko na zaɓen a ranar 6 ga watan Mayu mai zuwa.

A tsakiyar watan Janairun da ya gabata ne jam’iyyar Patriotic Salvation Movement (MPS) ta ayyana Mahamat Deby Itno a matsayin ɗan takararta a zaɓen shugaban ƙasa.

Deby Itno ya hau kan mulki ne a shekarar 2021 bayan mahaifinsa Idriss Deby Itno, wanda ya kwashe kusan shekara talatin a kan mulki, ya mutu a fagen yaƙi yayin fafatawa da wasu ƴan tawayen ƙasar.