Zan yi bakin kokari na don kada Buhari a zaben 2019- Atiku
Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar adawa ta PDP kuma tsohon Maitaimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya ce zai yi iya bakin kokarinsa don kada Shugaba Buhari daga mulki, a zaben shekarar 2019. Atiku ya bayyana hakan ne a jiya Laraba wajen wani taron shugabannin kabilar Igbo a Enugu. Atiku ya ce, ko dai ya […]
Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar adawa ta PDP kuma tsohon Maitaimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya ce zai yi iya bakin kokarinsa don kada Shugaba Buhari daga mulki, a zaben shekarar 2019.
Atiku ya bayyana hakan ne a jiya Laraba wajen wani taron shugabannin kabilar Igbo a Enugu.
Atiku ya ce, ko dai ya ci zabe ko ya fadi Shugaba Buhari ba zai ci gaba da mulkin Najeriya ba.