Zanga-zanga: Gwamnatin Katsina ta kira taron gaggawa
Taron ya gayyato kungiyoyi da sauran masu ruwa da tsakin da suka hada har da jami’an tsaro.
Gwamnatin Katsina ta kira taron masu ruwa da tsaki domin tattaunawa a kan batun zanga-zangar gama-gari da ake shirin gudanarwa a fadin Najeriya.
Taron wandan mukaddashin Gwamna kuma Mataimakin Gwamna, Faruk Jobe ya kira, na da nufin samo wata hanya domin daukar matakin bai-daya don ganin an samu zaman lafiya a jihar.
Taron ya gayyato kungiyoyi da sauran masu ruwa da tsakin da suka hada har da jami’an tsaro.
- Zanga-zangar tsadar rayuwa ta barke a Arewa
- HOTUNA: Yadda ’yan Arewa suka fara zanga-zangar tsadar rayuwa
- Majalisa za ta yi zaman gaggawa kafin zanga-zangar yunwa
A ranar Alhamis, 1 ga watan zanga-zanga ne ake sa ran fara zanga-zangar gama gari ta kwana 10 kan tsadar rayuwa a fadin Najeriya.
Akwai qarin bayani nan gaba>>>