Zanga-zanga ta barke a Kano kan yunkurin daukar matakin soji a Nijar

Daukar matakin yaki a Nijar rashin adalci ne da Turawan Yamma suka kitsa.

Zanga-zanga ta barke a Kano kan yunkurin daukar matakin soji a Nijar

Wasu masu zanga-zanga sun mamaye tituna a Jihar Kano suna bayyana adawa da yunkurin daukar matakin soji kan wadanda suka yi juyin mulki a Jamhuriyyar Nijar.

A kwanan nan ne Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ta bai wa dakarunta umarnin zama cikin shirin ko-ta-kwana domin warware tankiyar da ta kunnu a kasar da ke makwabtaka da Najeriya.

Aminiya ta ruwaito cewa, masu zanga-zangar dauke da tutocin Najeriya da Nijar sun fito a wannan Asabar suna masu bayyana adawarsu kan shirin tura dakarun Jamhuriyyar Nijar.

A yayin da suke tattaki a Kano, suna yekuwar cewa “al’ummar Nijar ’yan uwanmu ne da an riga an zama daya.

“Da mu da mutanen Nijar babu bambanci, ba ma son yaki.

“Daukar matakin yaki a Nijar rashin adalci ne da Turawan Yamma suka kitsa.”

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da kiraye-kiraye da gargadin daukar matakin soji a Nijar, musamman daga Arewacin Najeriya.

Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine

Madalla da hutu ga ’yan makaranta domin azumi

Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala

Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya