Zanga-zanga: Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi

Ana sa ran Shugaba Tinubu zai yi jawabi game da halin da ƙasar nan ke ciki.

Zanga-zanga: Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, zai yi wa al’ummar Najeriya jawabi a kafafen watsa labarai a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 na safe.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale ne, ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar da yammacin ranar Asabar.

Za a haska jawabin shugaban a kafafen yaɗa labarai daban-daban.

Wannan dai na zuwa ne bayan da aka shiga rana ta uku ta zanga-zangar kawo ƙarshen gurɓataccen shugabanci da kuma yunwa a ƙasar.

Zanga-zangar ta faro ne a ranar Alhamis a faɗin Najeriya.

A wasu jihohin an yi zanga-zangar cikin lumana ba tare da samun tashe-tashen hankula ba.

A jihohin Kano, Yobe, Borno, Jigawa, Katsina da sauransu an samu tashe-tashen hankula, lamarin da ya kai ga lalata kadarorin gwamnati da wawushe dukiyar al’umma.

Tuni aka sanya dokar hana fita a jihohin Kano, Borno da kuma Yobe.

Sai dai da safiyar ranar Asabar, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya sassauta dokar hana fita a jihar.

A Jihar Kano, kuwa al’amura na ci gaba da ta’azzara duk da dokar hana fita da gwamnatin jihar ta sanya.

NAJERIYA A YAU: Turka-Turkar Da Ta Dabaibaye Zaben Jihar Edo

Ambaliya ta shafi mutum miliyan 1.6 a Nijeriya — NEMA

Haɗurra 3 sun yi ajalin mutane 91 a kwanaki takwas — FRSC

Abba zai gina wa waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa gidaje a Kano