Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta

Zulum ya ce zai tallafa wa masarautar wajen gyara gine-ginen da Boko Haram suka lalata. 

Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya miƙa wa sabon Shehun Bama, Dakta Umar Kyari Umar El-Kanemi sandar sarauta, a wani biki da aka gudanar a filin wasa na garin Bama.

A yayin bikin, Gwamna Zulum ya yi alƙawarin kammala titin Maiduguri zuwa Banki domin bunƙasa harkokin kasuwanci tsakanin Najeriya, Kamaru da Chadi.

Haka kuma, ya ce gwamnatinsa za ta tabbatar da kammala Jami’ar Aikin Gona ta Tarayya da ke Bama da kuma dawo da wutar lantarki a yankin.

Zulum, ya ƙara da cewa za a ci gaba da tallafa wa masarautar da gyara gine-ginen da Boko Haram suka lalata.

Hakazalika, ya ce gwamnatinsa za ta taimaka wajen dawo da ’yan gudun hijira zuwa gidajensu.

A nasa jawabin, sabon Shehun Bama, Umar Kyari Umar El-Kanemi, ya gode wa gwamna Zulum bisa wannan matsayi da ya gaji daga mahaifinsa, Alhaji Ibrahim Umar Ibn Umar El-Kanemi, wanda ya shafe kusan shekaru 30 yana mulkin masarautar Bama.

An yi hawan dawaki, raye-rayen gargajiya, wake-wake da harbe-harben bindiga.

Manyan baƙi da suka halarta sun haɗa da Mataimakan Gwamnonin Borno da Yobe, Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, da sauran sarakuna da manyan jami’an gwamnati.

Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda

Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon Hadimi

Zulum ya bai wa sabon Shehun Bama sandar sarauta

Dokokin gyaran haraji sun tsallake karatu na biyu a majalisa