Zulum ya nada Dlakwa mukaddashin shugaban Jami’ar Jihar Borno

Gwamnan Borno, Babagana Zulum, ya amince da nadin Farfesa Haruna Dantoro Dlakwa a matsayin shugaban riko na Jami’ar Jihar Borno

Zulum ya nada Dlakwa mukaddashin shugaban Jami’ar Jihar Borno

Gwamnan Borno, Babagana Zulum, ya amince da nadin Farfesa Haruna Dantoro Dlakwa a matsayin shugaban riko na Jami’ar Jihar Borno da ke Maiduguri.

Nadin Dlakwa na kunshe ne a cikin wata sanarwa daga sakataren gwamnatin jihar Borno, Bukar Tijjani, a ranar Laraba.

Sanarwar ta ce amincewar Zulum ya biyo bayan shawarar da majalisar gudanarwar jami’ar ta bayar ne, bayan taronta na 10 da aka gudanar a ranar 15 ga Afrilu, 2024.

Kafin nadin nasa, Farfesa Dlakwa shi ne mataimakin shugaban jami’ar a bangaren ilimi.

Gwamna Zulum ya taya shi murna tare da fatan alheri zuwa lokacin da za a nada shguaban jami’ar.

Obasanjo na yunƙurin ɓata min suna don ɗan takararsa — Atiku

Sojoji sun kama masu garkuwa da mutane a Yobe

Na yi wa majinyata 15 magani — Likitan bogi

Rikicin fili: Gwamnatin Jigawa ta raba gonaki ga manoman iyakar ƙasa