NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Ƙananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
Hukumar UNICEF ta ce, kusan rabin yara a Najeriya suna fuskantar ƙalubale, kama daga cin zarafi zuwa rashin samun kulawa da dai sauran su
Najeriya tana cikin ƙasashen da suka fi yawan yara a duniya, a cewar Hukumar Kula da Ƙananan Yara ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF).
Sai dai a cewar Hukumar ta UNICEF, kusan rabin waɗannan yara suna fuskantar ƙalubale, kama daga cin zarafi zuwa rashin samun kulawa da dai sauran su.
Wadannan matsaloli da yara suke fuskanta dai sun daɗe suna ci wa masu ruwa da tsaki tuwo a ƙwarya.
- NAJERIYA A YAU: Yawan Kuɗaɗen Da Ake Bukata Don Samar Da ’Yan Sandan Jihohi
- DAGA LARABA: Shin kare kai daga harin ’yan ta’adda zai kawo karshen matsalar tsaro?
Yayin da ake bikin Ranar Yara ta Duniya, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kan halin da ya yara suke ciki a yau.
Domin sauke shirin, latsa nan