Yadda ake sayen kuri’u a Zaben Gwamnan Kogi

Wakilinmu ya ruwaito yadda jama’ar jihar ke tattauna yadda ake musu alkawairn N5,000 idan suka zabi dan takarar da aka yi musu tayi.

Yadda ake sayen kuri’u a Zaben Gwamnan Kogi

Daya daga cikin rumfunan zabe a Ekiti. An yi Allah-wadai da yadda ake sayen kuri’u

A yayin da ake gudanar da zaben gwamna a Jihar Kogi an samu rahotannin sayen kuri’u a wasu rumufuna.

Wakilinmu ya ruwaito yadda jama’ar jihar ke tattauna yadda ake musu alkawairn N5,000 idan suka zabi dan takarar da aka yi musu tayi.

Wakilinmu ya samu mutane na tattauna wannan batu a rumfar zabe da ke Miami daura da Adankolo a garin Lokoja  inda ya ga wakilin wata jam’iyya na sanya ido domin tabbatar da jam’iyyar da masu zabe suka dangwala wa kafin biyan su.

Irin haka na faruwa a Angwa Pawa da ke garin na Lokoja, inda ake kiran musamman mata gefe a ba su kudi, wasu tun kafin ma su yi zabe.

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan

A tabbatar an mutunta tsarin dimokuraɗiyya a Zaɓen Edo — Tinubu