’Yan bindiga sun hallaka mutum 46 a Neja

Harin ya fi muni a ƙauyen Konkoso, inda aka kashe aƙalla mutum 38 ta hanyar harbi ko kuma yankan rago. 

’Yan bindiga sun hallaka mutum 46 a Neja

’Yan bindiga sun hallaka aƙalla mutane 46 a wasu hare-hare da suka kai wasu ƙauyuka a Jihar Neja, inda suka yi wa wasu daga cikin waɗanda harin ya shafa yankan rago.

Kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya rawaito cewa lamarin ya faru a ranar Asabar, inda ’yan bindigar suka far wa garuruwa uku, cikinsu har da Tungan Makeri da Pissa da ke Karamar Hukumar Borgu, mai iyaka da Jihar Kwara.

Wata majiyar tsaro ta ce ’yan bindigar sun kai harin ne a kan aƙalla babura 41, kuma kowanne yana ɗauke da mutum biyu ko uku.

Bayanai sun ce harin ya fi muni a ƙauyen Konkoso, inda aka kashe aƙalla mutum 38 ta hanyar harbi ko kuma yankan rago.

Ana kuma fargabar cewa adadin waɗanda suka mutu a hare-haren zai iya zarta hakan, la’akari da cewa ’yan bindigar sun ƙone gidaje da dama da ba a san adadi ba.

Ko a farkon wannan wata na Fabarairu mahara sun kashe mutane sama da 160 a Jihar Kwara, wadda ita ma ke shiga cikin jerin jihohin arewacin Najeriya masu fama da tashe-tashen hankula daga ’yan ta’adda.

Sauran jihohin sun haɗa da Katsina da Zamfara da Kebbi da kuma Sakkwato.