Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen hasashen ruwan sama mai karfi da ka iya haifar da ambaliya a Jihohi 15 a yankin Arewacin Najeriya

Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA

Ambaliya a Afirka ta Kudu

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen ruwan sama mai karfi da zai iya haifar da ambaliya a jihohi 15 na Arewacin Najeriya da wasu wurare 68, a cikin kwanaki biyar masu zuwa.

Wannan gargadi ya fito ne daga Cibiyar Lura da Gargadin Ambaliya ta Kasa, karkashin Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, inda aka bukaci hukumomi da al’umma su dauki matakan gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi.

Cibiyar ta bayyana jerin jihohi da wuraren da ambaliyar za ta iya shafa sun hada da:

  • Adamawa: Jimeta, Mubi, Mayo-Belwa, Wuro-Bokki, Yola, Farkumo
  • Bauchi: Jama’a
  • Nasarawa: Keffi
  • Kaduna: Jaji, Kafanchan, Zaria, Birnin-Gwari
  • Katsina: Katsina, Bindawa, Kaita
  • Kebbi: Kamba, Kangiwa, Kalgo, Ribah, Sakaba, Saminaka, Gwandu, Jega, Bunza, Birnin Kebbi, Bagudo, Argungu
  • Kano: Bebeji, Gwarzo, Karaye, Sumaila, Tundun-wada
  • Niger: Rijau, Ibi, Chanchaga, Magama, Mashegu, Minna, Mokwa, New-Bussa, Sarkin Pawa, Wushishi
  • Taraba: Duchi
  • Jigawa: Miga, Ringim, Hadejia, Dutse
  • Yobe: Potiskum, Dapchi, Gasma, Gashua, Jakusko
  • Zamfara: Kaura Namoda, Maradun, Shinkafi, Bungudu, Gusau
  • Sokoto: Sokoto, Gagawa, Gada, Goronyo, Isa, Wamakko, Silame, Makira
  • Borno: Bama
  • Kwara: Jebba

Hukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.

Hukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.

Alkaluman da NEMA ta fitar sun nuna ceaw ambaliyar ta riga ta raba mutane 49,205 da muhallansu, ta lalata gidaje 10,663, da kuma gonaki 9,454 a al’ummomi daban-daban.

Jihohin da ibtila’in ya fi shafa sun hada da:

Imo (28,030), Ribas (22,345), Adamwa (12,613), Abia (11,907), Delta 8,810, Borno (8,164), Kaduna (7,334), Bayelsa (5,868) da Legas (5,793).
Sauran jihohin sun hada da Akwa Ibom (5,409), Niger (3,786), Ondo (3,735), Edo (3,234), Kogi (2,825), Sokoto (1,916), Kwara (2,663), Kano (1,446), Jigawa (1,428), Gombe (972), Anambra (925), da Babban Birnin Tarayya (1,025).

Mutanen sun kunshi maza 28,505 da mata 43,531, yara 62,393, tsofaffi 5,799 da nakassu 1,887.

Da haka hukumar ta bukaci jama’a da hukumomi da su dauki matakan gaggawa don rage illar ambaliya da kare lafiyar jama’a.