NAJERIYA A YAU: Hare-hare Kan Tarurrukan Siyasa Da Alakarsu da 2027
Ko hare-haren da ake kaiwa tarukan ‘yan siyasa manuniya ce ga abun da ka iya faruwa da zaben 2027?
Karuwar hare-hare kan ’yan siyasa a kwanan nan ta sa wasu ’yan Najeriya sun fara fargabar abin da ka iya faruwa idan aka fara yakin neman zaben 2027.
A kwanan nan ne dai wasu wadanda ake zargin ’yan bangar siyasa ne suka kai hare-hare a kan tarurruka ko kadarorin jam’iyyu ko ma daidaikun ’yan siyasa.
- NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Da Mutane Zasu Bi Wajen Neman Diyya
- DAGA LARABA: Yadda Matan Da Ke Auren Gwaji Suke Yamutsa Hazo
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan yadda siyasar 2027 za ta kasance duba da yadda hali yake a yanzu.
Domin sauke shirin, latsa nan